Wani jigo a jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP), Asiwaju Moshood Shittu, ya gargadi shugaban jam’iyyar na kasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, da ya guji yin gaggawar shiga duk wata kawance ko hadakar siyasa gabanin babban zabe na 2027.
Da yake magana da manema labarai a Abuja a karshen makon da ya gabata, Shittu, tsohon babban darakta (Arewa) na kungiyar yakin neman zaben shugaban kasa ta Kwankwaso, ya yi gargadin cewa duk wani hadaka da aka yi cikin gaggawa ba tare da wata manufa ko sahihin dan takarar shugaban kasa ba na iya zama “aure na rashin jin dadi.”
Ya kwatanta hakan da hadewar da aka yi a shekarar 2014 da ta kai ga hambarar da shugaba Goodluck Jonathan, yana mai cewa hakan ya haifar da mummunan sakamako na shugabanci.
Shittu ya shawarci Kwankwaso da ya yi nazari a tsanake, tare da nuna shakku kan sahihancin dan takarar, da tsarin hadakar, da tsarin tafiyar da mulki.
Ya jaddada cewa galibin kungiyoyin ‘yan adawa a Najeriya sun gaza ne saboda rashin daidaiton akida da hangen nesa.
Da yake kira ga Kwankwaso da ya fifita al’ummar Najeriya akan lissafin siyasa, Shittu ya yi gargadin cewa tarihi zai yanke hukunci da kakkausan harshe.
Ya karkare da cewa Najeriya ba za ta iya sake yin caca ba a cikin shugabancinta.