fidelitybank

NNPP ta gargaɗi Kwankwaso kan haɗakar jam’iyya

Date:

Wani jigo a jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP), Asiwaju Moshood Shittu, ya gargadi shugaban jam’iyyar na kasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, da ya guji yin gaggawar shiga duk wata kawance ko hadakar siyasa gabanin babban zabe na 2027.

Da yake magana da manema labarai a Abuja a karshen makon da ya gabata, Shittu, tsohon babban darakta (Arewa) na kungiyar yakin neman zaben shugaban kasa ta Kwankwaso, ya yi gargadin cewa duk wani hadaka da aka yi cikin gaggawa ba tare da wata manufa ko sahihin dan takarar shugaban kasa ba na iya zama “aure na rashin jin dadi.”

Ya kwatanta hakan da hadewar da aka yi a shekarar 2014 da ta kai ga hambarar da shugaba Goodluck Jonathan, yana mai cewa hakan ya haifar da mummunan sakamako na shugabanci.

Shittu ya shawarci Kwankwaso da ya yi nazari a tsanake, tare da nuna shakku kan sahihancin dan takarar, da tsarin hadakar, da tsarin tafiyar da mulki.

Ya jaddada cewa galibin kungiyoyin ‘yan adawa a Najeriya sun gaza ne saboda rashin daidaiton akida da hangen nesa.

Da yake kira ga Kwankwaso da ya fifita al’ummar Najeriya akan lissafin siyasa, Shittu ya yi gargadin cewa tarihi zai yanke hukunci da kakkausan harshe.

Ya karkare da cewa Najeriya ba za ta iya sake yin caca ba a cikin shugabancinta.

punch news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp