Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, NNPP, Dr. Rabi’u Musa Kwankwaso, ya ce jam’iyyarsa ta dukufa wajen ceto Najeriya daga matsalolin da take addabarta.
Kwankwaso, wanda ya bayyana haka a ranar Lahadin da ta gabata, yayin da yake kaddamar da ofishin yakin neman zaben NNPP na Kano, ya bukaci ‘yan Najeriya da su rika ganin NNPP a matsayin mai ceton su.
Sanata Kwankwaso ya dage cewa jam’iyyar ita ce ta fi dacewa a Najeriya, inda ya bukaci masu kada kuri’a da su tabbatar sun fito baki daya don amfani da ‘yancinsu.
Dan takarar ya dorawa ‘yan Najeriya da su yi wa kasar addu’a gabanin zaben 2023, inda ya kara da cewa jam’iyyarsa ta gabatar da mafi kyawu da zai taimaka wajen kwato kasar.
Ya ce, “an yi tarihi a Sharada inda wadanda ba su iya zuwa makaranta za a ba su dama kamar yadda ake sa ran sabuwar Najeriya.”
Ya kuma jaddada bukatar samar da hanyar ci gaba ga matasa tare da tabbatar wa matasa samun ingantacciyar gwamnati a karkashin jam’iyyar NNPP.
Shugaban jam’iyyar na jihar, Umar Haruna Doguwa ya ce dimbin jama’ar da suka halarci taron sun nuna yadda jam’iyyar za ta iya kaiwa ga nasara.