fidelitybank

NNPCL zai rage yawan man da ya ke baiwa matatar Ɗangote

Date:

Gwamnatin Tarayya na shirin rage yawan man fetur da take bai wa kamfanin Dangote Refinery daga ganga 300,000 kullum zuwa kasa da haka, sai idan yawan man da ake hakowa a Najeriya ya karu.

Wannan yunkuri na daga cikin shirin naira-for-crude don tabbatar da isasshen mai ga duka matatun mai na cikin gida, musamman ma bayan dawo da aikin matatun Port Harcourt da Warri, wadanda ke da jimillar damar tace ganga 135,000 a kullum.

Wannan matakin zai bai wa sauran matatun damar samun kaso daga ganga 450,000 da ake nufin bai wa matatun cikin gida.

Matatar Dangote, wadda ke buƙatar ganga 650,000 a kullum, tana samun ganga 300,000, amma wannan na iya raguwa saboda farfadowar matatun Warri da Port Harcourt, da wasu masu zuwa.

Karkashin Shirin Naira-for-Crude Gwamnati ta yanke shawarar sayar da danyen mai ga matatun cikin gida a naira maimakon dala, domin rage tasirin hauhawar darajar kudin kasashen waje.

Ana zargin cewa NNPC ba ta cika alkawarin isar da ganga 385,000 ga Dangote Refinery, wanda ke iya tilasta wa kamfanin ya sayi mai daga kasashen waje.

Hukumar NUPRC ami kula da hakar mai ta fitar da rahoto kan bukatar matatun mai na cikin gida daga watan Janairu zuwa Yuni 2025, inda ta bayyana cewa za a bukaci ganga 770,500 a kullum.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp