fidelitybank

NNPCL zai rage yawan man da ya ke baiwa matatar Ɗangote

Date:

Gwamnatin Tarayya na shirin rage yawan man fetur da take bai wa kamfanin Dangote Refinery daga ganga 300,000 kullum zuwa kasa da haka, sai idan yawan man da ake hakowa a Najeriya ya karu.

Wannan yunkuri na daga cikin shirin naira-for-crude don tabbatar da isasshen mai ga duka matatun mai na cikin gida, musamman ma bayan dawo da aikin matatun Port Harcourt da Warri, wadanda ke da jimillar damar tace ganga 135,000 a kullum.

Wannan matakin zai bai wa sauran matatun damar samun kaso daga ganga 450,000 da ake nufin bai wa matatun cikin gida.

Matatar Dangote, wadda ke buƙatar ganga 650,000 a kullum, tana samun ganga 300,000, amma wannan na iya raguwa saboda farfadowar matatun Warri da Port Harcourt, da wasu masu zuwa.

Karkashin Shirin Naira-for-Crude Gwamnati ta yanke shawarar sayar da danyen mai ga matatun cikin gida a naira maimakon dala, domin rage tasirin hauhawar darajar kudin kasashen waje.

Ana zargin cewa NNPC ba ta cika alkawarin isar da ganga 385,000 ga Dangote Refinery, wanda ke iya tilasta wa kamfanin ya sayi mai daga kasashen waje.

Hukumar NUPRC ami kula da hakar mai ta fitar da rahoto kan bukatar matatun mai na cikin gida daga watan Janairu zuwa Yuni 2025, inda ta bayyana cewa za a bukaci ganga 770,500 a kullum.

tribune news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp