fidelitybank

NNPCL ta fara tace danyen man fetur a matatar mai ta Fatakwal

Date:

Kamfanin samar da man fetur na ƙasar NNPCL ya fara kai ɗanyen man fetur don ayyukan tace mai na gwaji a matatar man fetur ta Fatakwal.

Jaridar Punch ta dai ambato wasu jami’ai na NNPCL na tabbatar mata da hakan, kuma ta ƙara da cewa dillalan man fetur su ma sun shaida mata wannan al’amari, da kuma cewa matatar za ta riƙa tace man fetur da dizal da kuma sauran nau’o’in mai don jihohin Najeriya 12 ciki har da Abia da Rivers da Akwa Ibom da Delta.

Ta ce NNPPCL ya shaida mata cewa nan gaba kaɗan za a kammala ayyukan tace mai na gwaji da ake yi a matatar Fatakwal, don fara tace ɗanyen man fetur da za a iya sayarwa a kasuwa.

A ranar 21 ga watan Disamba ne, gwamnatin Najeriya ta ba da sanarwar cewa an kammala wasu gyare-gyare a wani sashe da ake kira Area-5 na matatar Fatakwal da ke cikin jihar Rivers.

Ta ce ɓangaren farko na matatar ya kammala kuma za ta fara tace ɗanyen man fetur ganga 60,000 a kullum bayan hutun Kirsimeti.

Rahoton na zuwa ne yayin da ƙungiyar ƙwadago ta NLC a ranar Lahadi ta soki lamirin gwamnati saboda abin da ta kira gazawarta wajen cika alƙawurra da yawa da ta yi wa ‘yan Najeriya ciki har da alƙawarin cewa matatar man fetur ta Fatakwal za ta fara aiki a wannan wata na Disamba.

breaking news in nigeria today punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp