A ranar Alhamis ne kungiyar Dangote ta musanta rahotannin da ke cewa kamfanin man fetur na Najeriya, NPL, ya fara dauke mai daga matatarsa.
An bayyana cewa, NNPCL ya dauko man fetur daga matatar Dangote ya sayar wa ‘yan Najeriya kan Naira 897 kan kowace lita.
Rahoton ya zo ne a daidai lokacin da Shugaban Rukunin Dangote, Aliko Dangote ya bayyana cewa matatar man a shirye take ta fara hakowa da kuma sayar da albarkatun man fetur.
Sai dai Anthony Chiejina, Babban Jami’in Kula da Sana’o’i da Sadarwa na Rukunin Dangote ya ce har yanzu kamfanin na NNPC bai fara dauke mai daga matatar man ba.
A cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu, Chiejina ya ce: “An jawo hankalinmu ga wani kanun labarai ‘NNPCL na daga man Dangote, ana sayar da shi kan Naira 897 kan kowace lita’, wanda aka buga a jaridar Business Day na Laraba, 4 ga Satumba, 2024.
“Muna so mu bayyana cewa, NNPC bai fara dauke matatun man fetur na Dangote ba, PMS, wanda aka fi sani da man fetur daga matatar man Dangote.
“Saboda haka batun kayyade farashin man fetur da aka daga matatar man bai taso ba domin har yanzu ba mu kammala kwantiragin mu da NNPC ba.
“Kasuwar PMS tana da kayyadaddun tsari wanda duk ‘yan kasuwar mai da masu ruwa da tsaki a fannin suka sani, don haka ba za mu iya tantancewa, gyara, ko tasiri farashin kayayyakin, wanda ke karkashin kulawar hukumomin gwamnati da abin ya shafa.”NNPCL ba