Shugabannin ƙungiyoyin ƙwadago sun soki kamfanin rarraba wutar lantarki na (TCN) kan ƙorafi da damuwa da ya nuna sakamakon katsewar wutar lantarki da ta shafi ƙasar.
A wata sanarwa da NLC ta fitar, mai ɗauke da sa hannun shugabanta Joe Ajaero, ta ce daman kamar yadda ta sanar yajin aikin da ita ta takwararta suka kira na sai-baba-ta-gani a kan takaddamarta da gwamnatin tarayya kan gaza samar da sabon albashi mafi ƙanƙanta abu ne da daman zai shafi kusan kowace hukuma da kamfanoni ba TCN kadai ba.
Ƙungiyar ta musanta zargin da ta ce kamfanin wutar lantarkin ya yi na cewa mambobinta sun doki wasu ma’aikatan kamfanin a wasu wuraren.
Haka kuma sanarwar ta nuna damuwa kan yadda ta ce kamfanin na amfani da karfin soji wajen tilasta wa ma’aikatansa aiki, ta ce za ta dora alhakin duk wani rauni da ma’aikaci ya ji a kan kamfanin a sakamakon jibge sojoji a wasu wuraren aikin kamfanin.
Ƙungiyar ta ce, maganar kamfanin ya fito yana kokawa tare da nuna kamar ayyukansa kaɗai lamarin ya shafa bai dace ba