A baya-bayan nan ne hukumar hasashen yanayi ta Najeriya NIMET ta yi gargaɗin samun ambaliya a wasu jihohi 19 da ke ƙasar, sakamakon yadda ake samun mamakon ruwan sama a baya bayan nan.
Jihar Borno da ke arewa maso gabashin ƙasar da aka samu mummunar ambaliya a bara, na cikin jihohin da a yanzu ma ake hasashen za a iya samun ambaliyar.
Mahukunta a jihar na cewa tuni suka fara daukar matakan da suka kamata, don kaucewa faruwar hakan.
Sai dai domin fuskantar matsalar, mutane da dama a garin sun tashi tsaye wajen gudanar da ayyukan gayya musamman wajen buɗe magudanar ruwa da sauran su.