fidelitybank

Nijar za ta fuskanci mummunan sakamako idan Bazoum ya shiga wani hali – Tinubu

Date:

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yi gargadin “mummunan sakamako” idan gwamnatin mulkin sojan Nijar ta kyale lafiyar hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum ta kara ta’azzara yayin da ake yi masa daurin talala kamar yadda wata sanarwa da wani jami’in Turai ya fitar a ranar Juma’a.

A yayin wani kira ga shugaban Tarayyar Turai Charles Michel, shugaban Najeriya, Tinubu kuma shugaban kungiyar ECOWAS da ke adawa da juyin mulkin Nijar ya bayyana damuwarsa game da “tabarbarewar yanayin tsare shugaba Bazoum”.

A ranar 26 ga watan Yuli ne jami’an tsaron fadar shugaban kasar suka tsare tsohon shugaban mai shekaru 63 , wanda ke zaman juyin mulki karo na biyar a Nijar tun bayan samun ‘yancin kai daga Faransa a shekarar 1960.

Tinubu ya jaddada kudirin ECOWAS da kuma manufofin siyasa na daukar mataki daya. Duk da tasirin tattalin arzikin da wasu kasashen yankin ke fama da shi, ECOWAS za ta ci gaba da tabbatar da takunkumin, kamar yadda jami’in ya tabbatar.

Charles Michel ya jaddada cewa Tarayyar Turai za ta bai wa kungiyar ta ECOWAS cikakken goyon baya ba tare da kakkautawa ba, ya kuma yi Allah wadai da juyin mulkin da aka yi a Nijar ba bisa ka’ida ba.

Ya kuma ce Tarayyar Turai ta Æ™i amincewa da hukumomin da suka biyo bayan juyin mulkin tare da tabbatar da cewa shugaba Bazoum, wanda aka zaba bisa ka’ida, shi ne halastaccen shugaban kasar Nijar.

daily post news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp