fidelitybank

Nijar ta zargi Najeriya da yi mata zagon kasa

Date:

Gwamnatin Mulkin sojin Nijar ta tsaya kai da fata, cewa lalle makwabciyarta Najeriya na bayar da mafaka ga masu shirya mata zagon-ƙasa duk kuwa da musanta hakan da Najeriyar ta yi.

A ranar Lahadin da ta gabata ne shugaban gwamnatin mulkin sojan ta Nijar, Janar Abdourrahmane Tchiani ya yi zargin cewa, ƙasashen Benin da Najeriya da Chadi na hada baki da jami’an leken asiri na ƙasar Faransa don kifar da gwamnatinsa, zargin da gwamnatin Najeriya ta ce bai da tushe ko makama.

To amma a hirarsa da BBC, ministan harkokin Nijar Bakari Ya’u Sangare ya ce duk abin da Janar Tchiani ya fada gaskiya ne.

Ministan ya ce suna da tarin hujjoji na maganganun da suka yi kan cewa Najeriya na taimaka wa wajen yi mata zangon-ƙasa, ”muna da hanyoyin samun bayanai,” in ji shi.

A zargin da ya yi a baya shugaban mulkin sojin na Nijar ya ce wasau daga cikin Turawan da suka kora daga Nijar, suna nan cikin Najeriya suna horar da ‘yan ta’dda kuma suna taimaka musu da makamai da dabara iri-iri da za su tayar wa da Nijar hankali.

Najeriya dai ta buƙaci hukumomin na Nijar su ba ta cikakken bayani kan zargin da suke yi cewa akwai wani mutum da ke jagorantar yi wa Nijar din tawaye da ke da sansani a wasu jihohin kasar.

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp