fidelitybank

Nijar ta rage kasafin kuɗinta da kaso 40

Date:

Gwamnatin Nijar ta sanar da rage kashe kudaden da take shirin kashewa a shekarar 2023, inda ta rage kasafin kudinta da kashi 40 cikin dari.

Wannan shawarar ta zo ne bayan takunkumin da kasashen duniya suka kakaba wa kasar bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a watan Yuli.

Gwamnatin mulkin sojan ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da aka watsa ta gidan talbijin a ranar Asabar din da ta gabata.

Sojojin sun sanar da rage kasafin kudin daga dala biliyan 5.3 (£4.3bn) zuwa dala biliyan 3.2, duk da cewa ba a samu cikakkun bayanai na rage kuɗaɗen ba.

Akalla kashi 40 cikin 100 na tallafin kasafin kudin kasar Afirka ta Yamma ana sa ran zai fito ne daga abokan huldar waje.

Juyin mulkin da ya hamɓarar da shugaba Mohamed Bazoum ya janyo hukumomi kamar kungiyar ECOWAS da Tarayyar Turai da Amurka sun sanya takunkumi da datse kadarori, da rufe kan iyakokin ƙasar da kuma dakatar da kayan agaji.

Wadannan matakan sun haifar da tashin gwauron zabin abinci da karancin kayan masarufi, da suka hada da magungunan ceton rai.

Gwamnatocin sojoji da ke makwabtaka da Mali da Burkina Faso dai sun goyi bayan juyin mulkin Nijar.

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp