fidelitybank

Nijar ta kori ƴan ƙasar ta su tara wanda yanzu haka ba su da ƙasa

Date:

Shugaban mulkin sojin Nijar Abdourahamane Tchiani ya haramtawa wasu ƴan ƙasar mutum tara bayyana kan su a matsayin ƴan Nijar, bayan da ya ƙwace shaidar zama ƴan ƙasar na su.

Wadanda lamarin ya shafa sun haɗa da tsohon ministan ma’aikatar yawon buɗe ido,Rhissa Ag Boula, da Ighazer Hamidine Abdou.

Gwamnatin dai ta zarge su da aikata ta’addanci da cin amanar ƙasa da karya dokokin ƙasa.

A watan Agusta ne Janar Tchiani ya sanya wa dokar korar duk wani ɗan Nijar da aka samu da hannu wajen cin amanar ƙasar.

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan adam ta Human Rights Watch ta ce dokar wani salo ne na tauye haƙƙin ƴan ƙasar.

Hakan na nufin yanzu dai mutanen da aka kora din ba su da wata ƙasa da za su bayyana a matsayin ƙasarsu.

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp