fidelitybank

Nijar ta kori kamfanonin sadarwa na Faransa

Date:

A Jamhuriyar Nijar, gwamnatin mulkin sojan kasar ta sanar da korar kamfanonin sadarwa na ƙasar Faransa na Camusat da Aktivko a duk faɗin ƙasar.

Camusat na ɗaya daga cikin manyan kamfanonin sadarwa a Nijar, da kuma Aktivko wanda ya ƙware wajen samar da makamashi ga turakun sadarwa na wayoyin salula.

Wannan na zuwa ne a loƙacin da hukumomin mulkin sojan Nijar ke ci gaba da korar kamfanonin Faransa daga Nijar a ƙoƙarin raba gari da ita baki daya.

Wata sanarwa da Ministan Sadarwa Sidi Muhammad ya fitar ta ce an haramta wa dukkan ‘yan ƙasa yin aiki tare da kamfanonin, amma babu wani cikakken bayanin dalilin da ya sa gwamnatin ta ɗauki matakin a yanzu.

Sai dai masu lura da al’amuran yau da kullum a Nijar na cewa matakin ba zai rasa nasaba da tsaron ƙasa ba.

A gefe guda kuma, masu adawa da gwamnatin mulkin sojan na cewa haramcin yunƙuri ne kawai na kafa kamfanin da sojojin ke so.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta ɗaure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...
X whatsapp