Rundunar sojin Jamhuriyar Nijar ta bayyana cewa jami’anta sun kashe ƴan Lakurawa – waɗanda suka shiga ƙasar ta kudu maso yammaci, kamar yadda kafar Tamtan.info mai zaman kanta ta ruwaito a ranar 25 ga Nuwamba.
Rundunar ta ce sun kashe mayaƙan ƙungiyar a ranar 21 ga Nuwamba a Muntseka, na yankin Illela da ke kudu maso yammacin jihar Tahoua da ke kan iyakar ƙasa da Najeriya.
Rahoton ya ƙara da cewa, “ƴan ta’adda ne da ake kira Lakurawa ko Lukurawa da suka ɓulla a jihohin arewa maso yammacin Najeriya musamman, Kebbi da Sokoto da suke da iyaka da jihohin Jamhuriyar Nijar wato Dosso da Tahoua, inda suka kashe mutum 15.
“Wataƙila sun gudu ne daga Najeriya suka shiga Nijar domin tserewa daga yaƙarsu da sojojin Najeriya ke yi,” in ji rahoton.
Lakurawa sun ɗauki alhakin wasu hare-hare a jihohin Kebbi da Sokoto, kuma suna ikirarin alaƙa da ƙungiyar Ansaru wadda ke samun goyon bayan ƙungiyar al-Qaeda.