fidelitybank

Nijar ta bukaci Togo ta roki ECOWAS a sasanta

Date:

Gwamnatin sojan Nijar ta nemi shugaban ƙasar Togo, Faure Gnassingbe ya shiga tsakani a tattaunawa da ƙasashen duniya musamman ma ƙungiyar raya tattalin arzikin Afrika ta Yamma (Ecowas) wadda ta kakaɓa wa Nijar takunkumi tun bayan juyin mulki.

Ministan tsaron Nijar, Janar Salifou Mody ne ya bayyana haka lokacin da yake ganawa da Shugaba Gnassingbe a Lome babban birnin kasar ranar Litinin. Ya kuma nemi Togo ta tsayawa Nijar a yarjejeniyar janye sojojin Faransa daga kasar ta yankin Sahel.

“Yana da muhimmanci a koyaushe mu tunatar da abokan kawancenmu cewa, kofar Nijar a buɗe take, ko da an yi kulle-kullen da ba za mu iya magana da abokan hulɗarmu ba,” Mody ya shaida wa manema labarai bayan kammala taron.

Kungiyar Ecowas ta sanya wa Nijar takunkumin tattalin arziƙi da kuma rufe harkokin kasuwanci na kan iyaka da Nijar a yunƙurin matsa wa shugabannin kasar lamba har sai sun mayar da mulkin dimokradiyya.

Togo, duk da kasancewarta mamba a kungiyar Ecowas, ta dauki wasu matakai na hadin gwiwa da shugabannin sojojin Nijar tare da bayyana aniyar hawa teburin tattaunawa.

Tuni dai Faransa ta fara janye dakarunta 1,500 daga Jamhuriyar Nijar, bayan da gwamnatin mulkin sojan ƙasar ta buƙaci su fice jim kadan da hamɓarar da Shugaba Mohamed Bazoum a ranar 28 ga watan Yuli.

Ministan harkokin wajen Togo, Robert Dussey ya ce kasarsu a shirye take ta taimaka wajen tattaunawa.

“Togo na adawa da duk wani matakin juyin mulki” in ji shi. “Amma a yanayi na musamman na ƙasarku, Togo ta fahimta, kuma tana son taimaka muku.” in ji ministan

Shugaban Najeriyar, Bola Tinubu, wanda kuma shi ne jagoran Ecowas, ya bayyana taka-tsantsan wajen mu’amala da Nijar saboda damuwar da ake da ita dangane da hamɓaras da Shugaba Bazoum daga kan mulki.

Gwamnatin mulkin soja a Nijar ta ce za ta miƙa mulki bayan shekara uku hannun farar hula, yayin da ƙungiyar Ecowas ta buƙaci a gaggauta mayar da aiki da tsarin mulki.

Duk da haka, ana ci gaba da ƙoƙarin diflomasiyya don ganin a shawo kan lamarin.

assu update

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp