Mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo, a ranar Juma’a a Anambra, ya ce, kasancewar ya yi mataimakin shugaban kasa a shekaru bakwai da suka gabata tare da shugaban kasa, Manjo Janar Muhammadu Buhari (mai ritaya), ya gamsu cewa ,Allah ne ya zabe shi ya yi wa ‘yan Nijeriya hidima a matsayi na gaba.
Ya kuma bayyana cewa, nan ba da dadewa ba kokarin da gwamnatin Buhari ta yi na samar da tsaro zai bayyana nan da shekaru masu zuwa.
Osinbajo ya yi wannan jawabi ne a ranar Juma’a a Awka, babban birnin jihar Anambra, yayin da yake ganawa da wakilan jam’iyyar All Progressives Congress, a ci gaba da hulda da wakilan jam’iyyar da masu ruwa da tsaki a fadin kasar nan.
Wannan na zuwa ne a wata sanarwa da babban mataimaki na musamman ga mataimakin shugaban kasa kan harkokin yada labarai Laolu Akande ya sanyawa hannu a ranar Asabar mai taken ‘Yadda gwamnatin Buhari ke gyara tsarin tsaron Najeriya’.