fidelitybank

Ni ne uban matasa kuma su ne kaɗai zasu kawo canji a Najeriya – Obasanjo

Date:

Tsohon shugaban ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya ce, shi ne uban matasan Najeriya da ke cikin takaici, saboda tabarbarewar tattalin arzikin kasar.

Kamar yadda wani faifan bidiyo da ya ke zagayawa a shafukan sada zumunta ya nuna tsohon shugaban kasar ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da wasu matasa karkashin jagorancin Charles Chukwuemeka Oputa wanda aka fi sani da Charly Boy.

Charly Boy wanda ya yi ikirarin cewa shi ne shugaban matasan Najeriya masu takaici ya roki Obasanjo da ya ba da shawarar hanyoyin da za a bi don magance wahalhalun da ake fuskanta a kan matasan.

A cewar mawakin, matasan da suka hada da kansa sun riga sun shiga damuwa, saboda rashin aikin yi da ke karuwa.

Da yake magana, Obasanjo ya zargi shugabannin Najeriya da tabarbarewar tattalin arziki, yana mai cewa ba laifin Allah ba ne, amma masu mulki ne.

A cewarsa, hanya daya tilo da za a tabbatar da sauyi ita ce kafa gwamnati ta gari ta hanyar shugabanni nagari.

Ya bayyana kwarin gwiwar cewa, matasan suna iya kawo canjin da ake bukata, yana mai cewa “babu wanda zai yi sai matasa”.

“Kai ne shugaban matasan Najeriya masu takaici kuma ni ne mahaifinsu.

“Cewa mu talakawa da takaici ba laifin Allah bane illa zabin shugabannin mu ne idan kuma za ku canza hakan, ku canza al’amura, ku canza shugabanci. Mai tsafta da sauki,” Obasanjo ya kara da cewa.

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp