Tsohon Ministan Sufuri kuma dan takarar Shugaban kasa a karkashin Jamâiyyar APC, Hon. Chibuike Rotimi Amaechi, ya bayyana kansa a matsayin wanda ya fi kowa cancantar tsayawa takarar shugaban kasa, domin ya san matsalolin kasar nan kuma yana da karfin magance su idan ya zama shugaban kasa a zaben 2023 mai zuwa.
Babban kalubalen da ke addabar Najeriya shi ne batun rashin tsaro Amaechi ya ce yana da iya kuma a shirye yake ya yi amfani da kwarewarsa a tsawon shekaru a matsayinsa na kakakin majalisa da gwamnan jihar Rivers da kuma matsayinsa na minista wajen magance matsalolin.
Amaechi ya bayyana hakan ne a wata gajeriyar ganawar da ya yi da gwamna Abubakar Sani Bello da wakilai da magoya bayan jamâiyyar APC mai mulki a jihar Neja, inda ya jaddada cewa matsalar tsaro a jihar Ribas lokacin da yake Gwamna ya yi muni kamar yadda yake faruwa a Nijar a yau. amma ya samu damar dawo da zaman lafiya a jihar.