Jagoran jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na kasa, kuma dan takarar shugaban kasa, Bola Tinubu ya ce, shi ne ya yi gwagwarmayar da ta sa Muhammadu Buhari ya zama shugaban Najeriya.
Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi ga wakilan jam’iyyar APC gabanin zaben fidda gwani na jam’iyyar a Abeokuta, jihar Ogun.
Tsohon gwamnan na Legas ya kuma bayyana sarai cewa ya zabi Farfesa Yemi Osinbajo a matsayin abokin takarar Buhari.
Da yake karin haske kan yadda ya nada Osinbajo mataimakin shugaban kasa, Tinubu ya ce Buhari ya ba shi tikitin takarar mataimakin shugaban kasa, amma wasu jiga-jigan sun nuna rashin amincewarsu da batun tikitin musulmi da musulmi.
Ya ce a lokacin da aka neme shi da ya gabatar da sunayen mutane uku da za su tsaya takara, sai ya rubuta takardan takardan sunayen Yemi Kadoso, Wale Edun da Yemi Osinbajo. A cewar Naija News.
“Ba ku taɓa jin wannan daga gare ni ba. Wannan shi ne wuri na farko da nake fadin haka,” in ji Tinubu a harshen Yarbanci.
Akan bullar Buhari kuwa, Tinubu ya ce “Idan ba ni na jagoranci yakin ba, da Buhari ba zai fito ba. Ya yi takara na daya da na biyu da na uku, amma ya sha kaye. Har ma ya ce a talabijin ba zai sake tsayawa takara ba.
“Amma na je gidansa da ke Katsina, na ce masa za ka yi takara ka yi nasara, amma ba za ka yi wasa da batun Yarabawa ba. Tun da ya fito ba a nada ni Minista ba. Ban sami kwangila ba.
“A wannan karon, Yarbawa ce kuma a ƙasar Yarbawa, lokaci na ne.”
Shugaban APC ya kuma bayyana cewa Dapo Abiodun ya zama Gwamna saboda shi da Allah.
Ya ce: “Dapo da ke zaune a nan, zai iya zama Gwamna ba tare da ni ba? Muna filin wasa, sai suka yaga dukkan fastocinsa. Hatta tutar jam’iyya, ba su son a ba shi, ni ne na kawo.
“Idan yana son haduwa da Allah a daidai wurin da ya dace, lallai ne ya san cewa in ba ni da Allah ba, da bai zama Gwamna ba.”
Tinubu yana tare da gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo- Olu, da takwaransa na Kano, Umar Ganduje, da kuma tsohon gwamnan jihar Borno, Kasim Shettima.