fidelitybank

Ni na farfaɗo da siyasar Peter Odili a Rivers – Wike

Date:

Ministan Babban Birnin Tarayya kuma tsohon Gwamnan Jihar Rivers, Nyesom Wike, ya soki wanda ya gada, tsohon Gwamnan Jihar Rivers, Peter Odili, yana cewa shine ya farfado da shi a siyasar jihar bayan shafe shekaru a cikin halin koma baya.

Wike ya bayyana hakan ne a cikin wani faifan bidiyo da ya karade kafar sada zumunta ta X a ranar Lahadi.

Maganganun Wike sun biyo bayan kalaman da Odili ya yi na cewa Gwamna Siminilayi Fubara na Jihar Rivers ya hana Wike mayar da jihar tamkar mallakar kansa.

Da yake mayar da martani, Wike ya ce:
“Abin takaici ne abin da tsohon gwamna ya fada. Wannan mutumin da ya kamata ace dattijo ne kuma uba. Ya ce shugaban kasa ya hana wani dan siyasa, mutum daya da ke kokarin maida Jihar Rivers tamkar kadararsa.

“Kuna tuna lokacin da nake gwamna, Odili ya yabi ayyukana sosai. Har ma ya ce babu wani gwamna da ya hada ayyuka kamar yadda na yi. Me yasa a shekarar 2007, bayan ya bar mulki, bai iya kusantar mulki ba saboda Ameachi yana kan mulki? Ya kau. Amma lokacin da na zama gwamna a shekarar 2015, ni ne na dawo da shi cikin siyasa.”

Wike ya kara da cewa yana maida hankali kan aikinsa a matsayin Ministan Babban Birnin Tarayya.

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...
X whatsapp