Ɗan jarida kuma mawallafin mujallar Ovation Magazine, Dele Momodu, ya ce shi ne ɗan takarar shugaban ƙasa da matasa suka fi yayinsa a Najeriya.
Momodu ya bayyana hakan ne ranar Alhamis ta kafar talabijin ta Channels, jim kaɗan bayan ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar PDP mai adawa.
Da a ka tambaye shi ko zai iya ja da gogaggu kuma manyan ‘yan siyasa kamar su, Atiku Abubakar, Mista Momodu ya ba da amsa da cewa, shi a ka fi yayi a Najeriya.
“Ba na so na yi alfahari. Babu wanda ake yayi kamata, ni ne wanda aka fi yayi a Najeriya. Ba wai ina magana a cikin PDP ba,” in ji shi.
Tun farko Dele Momodu ya kai wa shugaban PDP na ƙasa, Ayorchia Ayu, ziyara a sakatariyar jam’iyyar da ke Abuja, inda ya miƙa masa wasiƙar nuna sha’awar tsayawa takarar a hukumance.
Ɗan jaridar ya yi takarar shugaban ƙasa a babban zaɓen 2011 ƙarƙashin jam’iyyar National Conscience Party (NCP). A cewar BBC.
A na sa ran gudanar da babban zaɓen a Najeriya cikin watan Fabarairu da Maris na shekarar 2023, inda PDP za ta nemi ƙwace mulki daga hannun APC ta Shugaba Buhari.