fidelitybank

Ni matasa suka fi yayi a kan Atiku – Dan takarar shugaban kasa a PDP

Date:

Ɗan jarida kuma mawallafin mujallar Ovation Magazine, Dele Momodu, ya ce shi ne ɗan takarar shugaban ƙasa da matasa suka fi yayinsa a Najeriya.

Momodu ya bayyana hakan ne ranar Alhamis ta kafar talabijin ta Channels, jim kaɗan bayan ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar PDP mai adawa.

Da a ka tambaye shi ko zai iya ja da gogaggu kuma manyan ‘yan siyasa kamar su, Atiku Abubakar, Mista Momodu ya ba da amsa da cewa, shi a ka fi yayi a Najeriya.

“Ba na so na yi alfahari. Babu wanda ake yayi kamata, ni ne wanda aka fi yayi a Najeriya. Ba wai ina magana a cikin PDP ba,” in ji shi.

Tun farko Dele Momodu ya kai wa shugaban PDP na ƙasa, Ayorchia Ayu, ziyara a sakatariyar jam’iyyar da ke Abuja, inda ya miƙa masa wasiƙar nuna sha’awar tsayawa takarar a hukumance.

Ɗan jaridar ya yi takarar shugaban ƙasa a babban zaɓen 2011 ƙarƙashin jam’iyyar National Conscience Party (NCP). A cewar BBC.

A na sa ran gudanar da babban zaɓen a Najeriya cikin watan Fabarairu da Maris na shekarar 2023, inda PDP za ta nemi ƙwace mulki daga hannun APC ta Shugaba Buhari.

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp