Minista Chibuike Rotimi Amaechi, ya jaddada biyayyarsa ga shugaban kasa Muhammadu Buhari da jam’iyyar APC a yunkurinsa na tsayawa takarar shugabancin Najeriya.
Amaechi ya bayyana haka ne a yayin wani taron tuntuba da shuwagabannin jam’iyyar, wakilai da sauran amintattun jam’iyyar a sakatariyar jam’iyyar APC reshen jihar Ribas a ranar Juma’a, inda ya nuna cewa, a yunkurinsa na zama shugaban kasa wanda ya cancanta, ba ya yanke kauna ko rashin aminci.
Amaechi ya bayyana bakin cikinsa cewa da yawa daga cikin ‘yan siyasa ba su fahimci manufar biyayya ba. “Aminci ba lokacin da ba a zaɓe ka ba ne, ka zama marar aminci. Aminci yana nufin ka bi mutumin da ya jagorance ka; cewa kun mika wuya ga shugabancinsa. Idan ba ku bi ba, yana nufin ba ku da aminci, kuna cin gajiyar mutumin ne kawai a siyasance da tattalin arziki. Ranar da ba zai iya ba ku gaskiyar tattalin arziki ba, ita ce ranar da kuka zama marasa aminci.
“Bari in gaya muku wani abu game da aminci. A shekarar 2007 muna cikin taro sai wani ya tambaye ni ko Dr. Peter Odili (tsohon gwamnan jihar Ribas) ya ce ba za ka yi takarar gwamna ba, me za ka yi? Na ce zan mika wuya in goyi bayan wanda ya amince da shi. Mun yi yakin neman na zama gwamna domin Dakta Odili ya kira ni ya ce ‘ka je kotu.’ Idan ba haka ba, mun hadu a kungiyance muka ce za mu tsaya a kan zabinsa. Amma ya kira ni ya ce ‘…a je kotu.’
A nasa bangaren, Shugaban jam’iyyar APC a jihar Ribas, Cif Emeka Beke, ya tabbatar wa Amaechi goyon bayan jam’iyyar da kuri’u a zaben fidda gwani na shugaban kasa.