fidelitybank

Ni har yanzu ban ga saƙon addu’a ba a imel ɗi na kamar yadda Akpabio ya bayyana – Sanata Kingibe

Date:

Sanata Ireti Kingibe mai wakiltar Babban Birnin Tarayya, FCT, Abuja a Majalisar Dattawa, ta ce ba ta samu wata ‘yar addu’a ba a cikin email din ta daga Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio.

Kingibe, Sanata a karkashin jam’iyyar Labour Party, LP, tana mayar da martani ga tabbacin Akpabio a yayin zaman taron na ranar cewa, an aika da “addu’o’i” ga ‘yan majalisar yayin da suke tafiya hutu.

Sanatan ta yi wannan magana ne a ranar Larabar da ta gabata yayin da take gabatar da shirin Siyasar Yau na Gidan Talabijin na Channels, inda ta ci gaba da cewa, ba ta samu wani alawus alawus da ya sabawa ka’ida ba.

“A’a, a gaskiya, ban sami wata addu’a ba, amma zan duba imel na don yin addu’a,” in ji Kingibe cikin raha, ta kara da cewa ba ta san tabbas abin da Akpabio ke magana akai ba.

Shugaban Majalisar Dattawan ya yi zaman Majalisar a ranar Larabar da ta gabata ya shaida wa Sanatocin cewa, “Don mu samu damar cin gajiyar hutun mu, magatakardan Majalisar ya aiko da wata alama zuwa asusunmu daban-daban”.

Daga baya Akpabio ya janye maganar, inda ya kwatanta kudaden da ake zaton an biya ne a matsayin “addu’o’i” da aka aika zuwa “akwatunan wasiku”.

Yayin da yake yarda da cewa yawancin mutane sun ɗauka cewa ƙila an biya su alawus-alawus ga ’yan majalisa, ya bayyana cewa irin waɗannan biyan kuɗi na iya zama abubuwan da suka dace da doka da za a biya mu.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp