fidelitybank

Ni da ‘yan Najeriya muna cikin farin cikin gyara matatar mai ta Fatakwal – Tinubu

Date:

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce “shi da ‘yan ƙasar suna cike da farin ciki” sakamakon gyara matatar mai ta garin Warri da kamfanin mai na NNPCL ya yi.

Wani saƙo da shugaban ya wallafa a shafinsa na X ya ce “hakan zai ƙara wa ‘yan Najeriya ƙwarin gwiwa kan fatan da suke da shi game da alƙawuran da muka yi”.

Ya ƙara da cewa labarin “hanya ce mai kyau ta kammala shekarar 2024 idan aka ƙara da nasarar da aka samu kan matatar mai ta Fatakwal”.

Yayin wani taron manema labarai a yau Litinin, shugaabn kamfanin NNPCL Mele Kyari ya bayar da sanarwar cewa sun gyara matatar kuma ta ci gaba da aiki a matakin kashi 60 cikin 100 na ƙarfinta.

A cewar Tinubu: “Tun da yanzu matatar Warri na aiki bisa kashi 60 cikin 100, tsarin gwamnatina na samar da tabbataccen makamashi yana kan hanya.

“Ina shawartar NNCPL ya hanzarta gyara matatar mai ta Kaduna da ɗaya matatar ta Fatakwal domin tabbatar da matsayin Najeriya wajen samar da makamashi a duniya.”

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...
X whatsapp