Tsohon shugaban Amurka, Donald Trump, ya musanta zargin da ake masa na neman murɗe sakamakon zaɓen 2020 da ya sha kayi.
Da ya bayyana a kotun birnin Washington, Mr Trump ya yi bayanin cikin sanyin murya, inda ya jaddada cewa bai aikata laifin da ake zarginsa da shi ba.
Ya shaidawa manema labarai cewa an gurfanar da shi ne saboda dalilan siyasa.
Wannan ne karo na uku da tsohon shugaban ƙasar ya bayyana a gaba kotu kan zargin aikata manyan laifuka. .
An ga Mr Trump yana dunƙule tafin hannunsa yayin da yake zaune a cikin kotun, ya kuma riƙa girgiza kai lokacin da ake karanto tuhumar. In ji BBC.