A yau Alhamis ne kwamitin kwararru na hukumar kwallon kafa ta Najeriya (NFF) zai gana domin tantance kociyoyin da suka nemi aikin horar da Super Eagles.
Bayan kammala tattaunawa, kwamitin zai gabatar da shawarwarin nasu ga kwamitin zartarwa na NFF.
Ana sa ran hukumar ta NFF za ta bayyana wanda ya yi nasara bayan haka.
Manyan kociyoyin da suka hada da Emmanuel Amuneke da Finidi George da Daniel Amokachi da Samson Siasia da Salisu Yusuf duk sun nemi ya jagoranci Super Eagles.
Tsohon kociyan kungiyar Indomitable Lions na Kamaru, Antonio Conceicao shi ma yana cikin masu neman babban mukami.
Ana kuma sa ran kwamitin fasaha zai gabatar da bukatar masu horas da ‘yan wasan na neman kujerar da babu kowa a kungiyar ta Golden Eaglets.