Hukumar kwallon kafa ta kasa (NFF), ta yi wa Jose Peseiro tayin albashin dala 50,000 domin ya ci gaba da zama kocin Super Eagles.
Kwantiragin Peseiro na baya ya kare ne a karshen gasar cin kofin kasashen Afirka na 2023 a Cote d’Ivoire.
Mai horaswar na Portugal din ya cimma burin da hukumar NFF ta sanya masa a wasan kusa da karshe.
“Hukumar NFF ta ba shi albashin dala 50,000 duk wata saboda abin da za su iya kenan,” wata majiya mai karfi ta shaida wa SCORENigeria.
“Kwallo yanzu tana gaban kociyan don karbar wannan ko kin amincewa.”
Kwanan nan Peseiro ya bayyana cewa yana da akalla tayi bakwai daban-daban daga kungiyoyin kasa da kungiyoyi kuma zai yanke shawarar makomarsa a cikin kwanaki masu zuwa.
An nada dan wasan mai shekaru 63 a matsayin kocin Super Eagles a ranar 15 ga Mayu, 2022.