Hukumar kwallon kafa ta Najeriya NFF, ta bayyana takaicinta kan tarzomar da ta biyo bayan wasan neman shiga gasar cin kofin duniya da kungiyar kasar ta Super Eagles ta yi da Black Stars ta Ghana jiya Talata a filin wasa na tunawa da Mashood Abiola da ke Abuja inda aka tashi 1-1.
Ta kuma bayyana alhini kan mutuwar wani jami’in hukumar kwallon kafa ta CAF a yayin wasan, tare da musanta ikirarin cewa tarzomar da aka samu ce ta yi sanadin mutuwarsa.
Sakatare Janar na hukumar ta NFF, Muhammad Sanusi, ya shaida wa BBC cewa, suna bai wa ‘yan Najeriya hakuri kan sakamakon wasan da ba kasar rashin cancantar shiga gasar cin kofin duniya ta bana da za a yi Qatar.