fidelitybank

NFF ta naɗa ɗan ƙasar Portugal a matsayin kocin Eagles

Date:

Hukumar kwallon kafa ta Najeriya NFF ta bayar da sanarwar naɗa Jose Peseiro a matsayin sabon kocin Super Eagles.

Hukumar ta ce, Jose Peseiro wanda ɗan asalin ƙasar Portugal ne shi zai jagoranci Super Eagles. In ji BBC.

NFF ta sanar da matakin ne cikin wata sanarwa daga kakakinta Ademola Olajire.

Sanarwar ta ce zai fara jagorantar tawagar Super Eagles a ziyarar da za ta kai Amurka a wasannin sada zumunci.

Tsohon dan wasan Super Eagles Finidi George da Salisu Yusuf za su zama mataimakan sabon kocin.

Tun a watan Disamba Hukumar ƙwallon Najeriya ta fara sanar da naɗa kocin amma daga baya ta naɗa Augustine Eguavoen a matsayin kocin rikon kwarya domin ya ja ragamar Super Eagles a gasar cin kofin Afirka.

A watan Disamban 2021 NFF ta ce kwamitin zartarwata ne ya amince da naɗa Peseiro kuma zai zama mai sa ido kafin a dawo ya ci gaba.

Amma daga baya hukumar ta ce ta fasa saboda kwazon Augustine Eguavoen

legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram Takwas a jihar Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun kashe aƙalla...

Sauya sunan Kwaleji a Oyo ya fusata Dalibai

Ɗaliban kwalejin fasaha ta Ibadan sun gudanar da zanga-zanga...

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Dantata

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta'aziyya...

Trump ba shi da hankali ko tunani a kan harajin sa – Elon Musk

Tsohon mai ba shugaban Amurka Donald Trump shawara kan...

Dangote ya rage man fetur lita 840

Matatar man Dangote ta rage farashin litar man fetur...

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...
X whatsapp