Sashen bunkasa alkalan wasa na hukumar kwallon kafa ta Najeriya ta kori alkalin wasa Jimoh Abdurasheed da mataimakinsa Zakari Adamu daga ci gaba da alkalan wasa a gasar Premier ta Najeriya.
Alkalan wasan biyu sun jagoranci wasan ranar 24 da suka hada Rivers United da Kano Pillars a filin wasa na Adokiye Amiesimaka a karshen makon da ya gabata.
Kungiyoyin biyu sun fafata ne da ci 1-1 a wasan.
An dauki matakin ne bayan da kungiyar Kano Pillars ta kai karar hukumar NPFL.
An ce jami’an sun shiga wani hali na rashin da’a wanda ya sa Rivers United ta farke a karawar.
An ce an sanar da matakin na sallamar jami’an ne ga shugaban NFF da babban sakatare.