Hukumar kwallon kafa ta Najeriya NFF ta sanar da nadin Jose Peseiro, a matsayin sabon mai horas da Super Eagles.
Hukumar kwallon kafa ta kasa NFF ta sanar da nadin Peseiro dan kasar Portugal, a matsayin sabon mai hioras da tawagar kungiyar kwallon kafa ta Super Eagles.
Sai dai hukumar ta NFF ta ce, Augustine Eguavoen, wanda a ka nada kocin rikon kwarya bayan sallamar Gernot Rohr a makonnin da su ka gabata, zai jagoranci Super Eagles zuwa gasar cin kofin Afrika da za a fara ranar 9 ga watan Janairu a Kamaru.
A cikin wata sanarwa da hukumar ta NFF ta sanar, bayan yin nazari a kan takardar da shugaban kwamitin zartaswa ya gabatar, ya amince da kudirin nada Mista Jose Peseiro a matsayin sabon kocin Super Eagles, bayan kawo karshen dangantaka da Gernot Rohr.
Duk da haka, kwamitin ya yanke shawarar cewa, Augustine Eguavoen, wanda ya nada babban kocin rikon kwarya, zai jagoranci Super Eagles zuwa gasar AFCON 2021 a Kamaru tare da Mista Peseiro.