fidelitybank

NFF ta ƙara sabunta kwantiragin Peseiro – Tayo

Date:

Shugaban wasanni Tayo Adeyemo ya bukaci hukumar kwallon kafa ta Najeriya, NFF, da ta rike kocin Super Eagles, Jose Peseiro.

Ya ce tsawaita kwantiragin Paseiro zai taimaka wa Super Eagles wajen tunkarar gasar AFCON na gaba.

Adeyemo ya bayyana haka ne a ranar Laraba a Legas yayin da yake zantawa da NAN.

Ya kuma bukaci hukumar ta NFF da ta mayar da hankali wajen fitar da ‘yan wasan gida da za su lashe gasar cin kofin Afrika na gaba, AFCON, da za a yi a Morocco.

“Morocco za ta karbi bakuncin gasar cin kofin nahiyar Afirka karo na 35 na Total Energies CAF ko kuma gasar cin kofin Afrika a shekarar 2025. Ya kamata NFF ta tsawaita kwantiragin kocin,” in ji shi.

Ya bukaci Super Eagles da NFF su mayar da hankali kan gasar AFCON na gaba da wasannin share fage idan har kungiyar ta zarce tarihin da ta samu a baya.

Adeyemo ya ce kungiyar na bukatar karin ‘yan wasa kwazo da kwarewa da jajircewa domin lashe kofin a yunkurinsu na gaba.

Ya ce: “Ya kamata su kara yin shiri kan horo da buga wasannin sada zumunta akai-akai tare da ‘yan wasan gida idan ‘yan wasan duniya ba su shirya ba.”

Adeyemo ya ce Super Eagles ta yi rawar gani wajen samun matsayi na biyu a gasar AFCON ta 2023 da Cote d’Ivoire ta karbi bakunci.

“Kafin gasar da yawa daga cikin ‘yan Najeriya ba su yi tsammanin kungiyar za ta kai wasan karshe ba ko ma ta tsallake zuwa matakin rukuni.

“Don kungiyar ta kai wasan karshe, hakan na nufin kociyan ya taka rawar gani, kuma ya kamata a ci gaba da rike shi,” in ji shi.

legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp