Neymar ba zai buga wasanni biyu na gasar cin kofin duniya da Brazil za ta buga ba, bayan da ya samu rauni a kafarsa ta dama, in ji likitan tawagarsu.
An maye gurbin dan wasan mai shekaru 30 a minti na 80 na wasan da suka doke Serbia da ci 2-0 a ranar Alhamis, bayan da Nikola Milenkovic ya yi masa ya yi masa keta.
Shi ma Danilo ba zai buga wasanni biyu masu zuwa ba saboda rauni a idon sawunsa.
“Neymar da Danilo sun yi gwajin MRI a ranar Juma’a da yamma kuma mun sami rauni a idon sawun su biyu,” in ji likitan tawagar Brazil Rodrigo Lasmar.
Da yake magana bayan nasarar da suka yi da Serbia, babban kocin Brazil Tite, ya ce, suna da yakinin cewa Neymar zai ci gaba da taka leda a gasar cin kofin duniya.
Dan wasan na Paris St-Germain ya samu raunuka da dama da kafarsa ta dama a shekarun baya.