Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya sha alwashin mayar da mummunan martani kan harin makami mai linzami da ƴan tawayen Houthi suka kai kusa da wani filin jirgin sama a Isra’ila.
A cikin wani bidiyo da aka wallafa a shafukan sada zumunta, Netanyahu ya yi barazanar far wa ƙungiyar, inda ya ce: “Mun kai hari a baya, za mu kuma sake kai hari a gaba”.
Makamin mai linzami da ƴan Houthi waɗanda ke samun goyon bayan Iran suka harba daga Yemen, ya faɗa kusa da filin jirgin sama a Ben Gurion ranar Lahadi da safe, a cewar hukumomi.
Lamarin ya jikkata mutum huɗu, yayin da wasu biyu suka jikkata a kan hanyar su ta zuwa wani matsuguni, a cewar kafofin yaɗa labaran Isra’ila.
Mai magana da yawun sojojin Houthi, Yahya Saree ya bayyana a wata sanarwa da aka watsa a gidan talabijin cewa “yanzu filin jirgin saman Isra’ila ba shi da tsaron da za a iya yin tafiye-tafiye”.
Ministan tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya faɗa a wata sanarwa cewa: “Duk wanda ya kawo mana hari, za mu mayar da martani har sau bakwai”.