fidelitybank

Netanyahu ya sha alwashin mayar da martani kan harin da ƴan Houthi suka kai

Date:

Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya sha alwashin mayar da mummunan martani kan harin makami mai linzami da ƴan tawayen Houthi suka kai kusa da wani filin jirgin sama a Isra’ila.

A cikin wani bidiyo da aka wallafa a shafukan sada zumunta, Netanyahu ya yi barazanar far wa ƙungiyar, inda ya ce: “Mun kai hari a baya, za mu kuma sake kai hari a gaba”.

Makamin mai linzami da ƴan Houthi waɗanda ke samun goyon bayan Iran suka harba daga Yemen, ya faɗa kusa da filin jirgin sama a Ben Gurion ranar Lahadi da safe, a cewar hukumomi.

Lamarin ya jikkata mutum huɗu, yayin da wasu biyu suka jikkata a kan hanyar su ta zuwa wani matsuguni, a cewar kafofin yaɗa labaran Isra’ila.

Mai magana da yawun sojojin Houthi, Yahya Saree ya bayyana a wata sanarwa da aka watsa a gidan talabijin cewa “yanzu filin jirgin saman Isra’ila ba shi da tsaron da za a iya yin tafiye-tafiye”.

Ministan tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya faɗa a wata sanarwa cewa: “Duk wanda ya kawo mana hari, za mu mayar da martani har sau bakwai”.

sspdf news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp