fidelitybank

NERC ta ci tarar kamfanin AEDC naira biliyan 1.69 kan tsauwala kuɗin wuta

Date:

Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Najeriya (NERC) ta ci kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Abuja (AEDC) tarar Naira Biliyan 1.69 bisa laifin tsauwala wa abokan hulɗarsu kuɗin wuta

Gidan talbijin na Channels ya rawaito cewar tarar ta ta’allaka ne a kan rashin bin umarnin da hukumar ta bayar a baya na iyakance kiyasin lissafin kuɗi ga masu amfani da wutar lantarki.

Hukuncin, wanda aka zayyana a cikin takarda mai suna ‘Order NERC/2024/114’, wani ɓangare ne na umarnin hukumar na watan Satumba na shekarar 2024.

Umurnin mai kwanan watan Agusta 30, ya samu sa hannun mataimakin shugaban NERC Musiliu Oseni da kwamishinan shari’a da lasisi da bin doka, Dafe Akpeneye.

Tarar ta fito ne ta shafin intanet na NERC kamar yadda gidan talabijin na Channels ya ruwaito.

Binciken da NERC ta yi kan tsarin biyan kudi na AEDC ya nuna cewa kamfanin tsalawa kwastomomi fiye da kima a tsakanin watan Janairu zuwa Satumba na 2023.

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp