fidelitybank

NEMA za ta fara ƙwashe mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa – Zubaida

Date:

Darakta-Janar ta Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa, NEMA, Zubaida Umar, ta ce, hukumar ta fara shirin aikin kwashe jama’ar da ke fuskantar barazanar ambaliyar ruwan sama zuwa kan tudu.

A daidai lokacin da a ke ci gaba da fuskantar mamakon ruwan sama, NEMA ta ce ambaliyar ruwa ta shafi jihohi 28, inda mutum 175 suka mutu, sannan mutum 207,902 suka rasa muhallansu.

Hukumar ta ce ambaliyar ta shafi mutum 526,703 a ƙananan hukumomi 133, inda lamarin ya shafi gidaje 79,138 da kuma hekta 106,178 na gonaki.

Domin fuskantar wannan yanayin ne, gwamnonin jihohi da NEMA ta fara kwashe mutane daga wuraren da suke fuskantar barazanar ambaliyar domin rage ɓarnar.

Ta ƙara da cewa NEMA za ta buɗe cibiyoyinta domin sauƙaƙa ayyukan hukumar domin jiran kar ta kwana.

Wannan na zuwa ne bayan ziyarar Shugaban Ma’aikatan Gidan Gwamnatin Najeriya, Femi Gbajabiamila a hukumar, inda ya je domin duba yadda ake gudanar da ayyukan hukumar bayan wani taron ƙara wa juna sani da ya yi da hukumomin da ke ƙarƙashin Fadar Shugaban Ƙasa.

Darakta-Janar ɗin ta kuma buƙaci ƙarin haɗin kai daga kwamitin majalisa da sauran masu ruwa da tsaki domin faɗaɗa ayyukan NEMA da shirye-shiryenta na fuskantar ayyukan agajin gaggawa.

breaking news in nigeria today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp