fidelitybank

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 144 daga Nijar

Date:

Hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa NEMA, ta ce ta karɓi ƙarin rukuni na ƴan Najeriya 144 waɗanda suka maƙale a Jamhuriyar Niger.

Kodinetan hukumar a jihar Kano, Nuraddeen Abdullahi, shi ya bayyana hakan yayin da yake karɓar mutanen a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano da ke jihar Kano. Mutanen sun iso gida ne da misalin karfe 2:30 na rana.

Ya ce an mayar da mutanen ne karkashin wani shiri na Hukumar Kula da Ƴan Cirani ta Duniya daga Niamey, babban birnin ƙasar.

Mutanen sun haɗa da maza 106 da mata 16 da kuma yara 22.

Mista Abdullahi ya ce mutanen da aka dawo da su ɗin sun fito ne daga sassan ƙasar da dama – wasu daga Kano da Kaduna da Katsina da Abia da Sokoto da Edo – da sauransu.

A cewarsa, za a horar da mutanen kan sana’o’i daban-daban tare da ba su jari domin dogaro da kansu.

Kodinetan ya shawarci ƴan Najeriya da su daina saka rayukansu cikin haɗari ta hanyar tafiye-tafiye da nufin samun ingantaccen rayuwa a wasu ƙasashe, inda ya ce ba ƙasar da tafi Najeriya.

Kamfanin Dillanicin Labaran Najeriya ya ruwaito cewa tsakanin watan Febrairu da Maris, an an dawo da ƴan Najeriya 300 zuwa gida waɗanda suka maƙale a Nijer.

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp