fidelitybank

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 144 daga Nijar

Date:

Hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa NEMA, ta ce ta karɓi ƙarin rukuni na ƴan Najeriya 144 waɗanda suka maƙale a Jamhuriyar Niger.

Kodinetan hukumar a jihar Kano, Nuraddeen Abdullahi, shi ya bayyana hakan yayin da yake karɓar mutanen a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano da ke jihar Kano. Mutanen sun iso gida ne da misalin karfe 2:30 na rana.

Ya ce an mayar da mutanen ne karkashin wani shiri na Hukumar Kula da Ƴan Cirani ta Duniya daga Niamey, babban birnin ƙasar.

Mutanen sun haɗa da maza 106 da mata 16 da kuma yara 22.

Mista Abdullahi ya ce mutanen da aka dawo da su ɗin sun fito ne daga sassan ƙasar da dama – wasu daga Kano da Kaduna da Katsina da Abia da Sokoto da Edo – da sauransu.

A cewarsa, za a horar da mutanen kan sana’o’i daban-daban tare da ba su jari domin dogaro da kansu.

Kodinetan ya shawarci ƴan Najeriya da su daina saka rayukansu cikin haɗari ta hanyar tafiye-tafiye da nufin samun ingantaccen rayuwa a wasu ƙasashe, inda ya ce ba ƙasar da tafi Najeriya.

Kamfanin Dillanicin Labaran Najeriya ya ruwaito cewa tsakanin watan Febrairu da Maris, an an dawo da ƴan Najeriya 300 zuwa gida waɗanda suka maƙale a Nijer.

daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp