Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana cewa an kammala biyan kudin jarabawar hukumar shirya jarabawa ta kasa wato NECO a shekarar 2022, inda ta ce za a fitar da sakamakon a karshen wata.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwar manema labarai da kwamishinan yada labarai na jihar, Hon. Ibrahim Magaji Dosara.
Kwamishinan ya shawarci iyaye da masu kula da ‘yan takarar da suka zana jarabawar NECO ta 2022 da su tuntubi makarantunsu domin samun sakamakonsu a karshen watan Satumban 2022.
Ya yi nuni da cewa, don haka ya kamata wadanda abin ya shafa su rika samun sakamakonsu ta yanar gizo domin samun gurbin karatu a manyan makarantun gaba da sakandire kafin a fitar da takardar zuwa makarantu daban-daban daga hukumar shirya jarabawar ta jihar Zamfara.
Dosara, ya kuma yi kira ga iyaye da masu kula da su da su kara hakuri saboda ana ci gaba da tattaunawa don fitar da sakamakon jarabawar NECO na 2021.
Sanarwar ta kara da cewa, “Gwamnatin jihar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen ganin an farfado da fannin ilimi a jihar ta hanyar sauye-sauye daban-daban.”