Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta NECO, ta fitar da sakamakon jarrabawar wannan shekara.
Hukumar ta ce sakamakon ya nuna kashi 60.55 na ɗaliban da suka rubuta jarrabawar sun samu kiredit biyar zuwa sama ciki har da daraussan Turanci da Lissafi.
Shugaban hukumar, Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai da ya gudanar a shalkwatar hukumar ta NECO da ke garin Minna na jihar Neja.
Farfesa Wushishi ya ce ɗalibai miliyan ɗaya da dubu ɗari uku da sittin da ɗari huɗu da ashirin da uku (1,376,423), ne suka rubuta jarrabawar ta bana.
”Daga cikin wannan adadin akwai maza 706,950 sai kuma mata 669,473”, in ji shi.
”Adadin ɗaliban da suka samu kiredit biyar zuwa sama ciki har da darussan Lissafi ta Turanci shi ne 828,284, waɗanda kuma suka samu kiredit biya zuwa sama ba tare da la’akari da darussan Turanci da Lissafi ba ya kai 1,147,597”, in ji shugaban na NECO.
Dangane da batun satar jarrabawa kuwa, Farfesa Wushishi ya ce a wannan shekarar an samu gagarumar raguwar matsalar idan aka kwatantwa da shekarar da ta gabata.