fidelitybank

NECO ta fitar da sakamakon jarrabawar 2024

Date:

Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta NECO, ta fitar da sakamakon jarrabawar wannan shekara.

Hukumar ta ce sakamakon ya nuna kashi 60.55 na ɗaliban da suka rubuta jarrabawar sun samu kiredit biyar zuwa sama ciki har da daraussan Turanci da Lissafi.

Shugaban hukumar, Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai da ya gudanar a shalkwatar hukumar ta NECO da ke garin Minna na jihar Neja.

Farfesa Wushishi ya ce ɗalibai miliyan ɗaya da dubu ɗari uku da sittin da ɗari huɗu da ashirin da uku (1,376,423), ne suka rubuta jarrabawar ta bana.

”Daga cikin wannan adadin akwai maza 706,950 sai kuma mata 669,473”, in ji shi.

”Adadin ɗaliban da suka samu kiredit biyar zuwa sama ciki har da darussan Lissafi ta Turanci shi ne 828,284, waɗanda kuma suka samu kiredit biya zuwa sama ba tare da la’akari da darussan Turanci da Lissafi ba ya kai 1,147,597”, in ji shugaban na NECO.

Dangane da batun satar jarrabawa kuwa, Farfesa Wushishi ya ce a wannan shekarar an samu gagarumar raguwar matsalar idan aka kwatantwa da shekarar da ta gabata.

the sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp