fidelitybank

Ndume ya sa alamar ayar tambaya kan gaggawar amincewa da ƙudurin harajin Tinubu

Date:

Sanata Ali Ndume mai wakiltar Borno ta kudu ya ɗiga alamar tambaya kan yadda ake gaggawa domin amincewa da ƙudurin harajin da shugaban ƙasa Tinubu ya aika majalisa.

Ndume ya bayyana hakan ne a tattaunawarsa da tashar Channels a shirin Politics Today.

Sanatan ya ce a zaɓen 2023, sanatoci 25 ne kawai suka dawo, wanda hakan a cewarsa ke nuna cewa mutane sun fara daina amince da su.

Ya ƙara da cewa yadda ake gaggawar amincewa da ƙudurin na harajin, ya nuna kamar akwai lauje cikin naɗi.

“Ba wai ina da matsala da ƙudurin ba ne, kuma ba wai ina cewa a yi watsi da shi ba ne baki ɗaya, amma tunda gwamnoninmu waɗanda su ne jagororinmu da kuma majalisar tattalin arziki da wasu ɗaiɗaikun mutane sun bayyana cewa akwai buƙatar ƙarin lokaci domin a tattauna, ya kamata a ɗan ƙara lokaci. Me ya sa ake gaggawa?” in ji shi.

Ndume ya ce babbar matsalarsa da ƙudurin ita ce lokacin da aka bijiro da ita, inda a cewarsa bai kamata a ce an kawo maganar ƙudurin ba a daidai wannan lokacin da ƴan Najeriya suke cikin ƙuncin rayuwa.

“Tun kakanninmu uuna biyan haraji a arewa. Don haka ba wai muna tsoron biyan haraji ba ne, duk wani ɗan ƙasa na ƙwarai zai biya haraji, amma gaskiya zuwa da wannan maganar a wannan lokacin bai dace ba,” in ji shi.

dailypost news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp