fidelitybank

Ndume ya sa alamar ayar tambaya kan gaggawar amincewa da ƙudurin harajin Tinubu

Date:

Sanata Ali Ndume mai wakiltar Borno ta kudu ya ɗiga alamar tambaya kan yadda ake gaggawa domin amincewa da ƙudurin harajin da shugaban ƙasa Tinubu ya aika majalisa.

Ndume ya bayyana hakan ne a tattaunawarsa da tashar Channels a shirin Politics Today.

Sanatan ya ce a zaɓen 2023, sanatoci 25 ne kawai suka dawo, wanda hakan a cewarsa ke nuna cewa mutane sun fara daina amince da su.

Ya ƙara da cewa yadda ake gaggawar amincewa da ƙudurin na harajin, ya nuna kamar akwai lauje cikin naɗi.

“Ba wai ina da matsala da ƙudurin ba ne, kuma ba wai ina cewa a yi watsi da shi ba ne baki ɗaya, amma tunda gwamnoninmu waɗanda su ne jagororinmu da kuma majalisar tattalin arziki da wasu ɗaiɗaikun mutane sun bayyana cewa akwai buƙatar ƙarin lokaci domin a tattauna, ya kamata a ɗan ƙara lokaci. Me ya sa ake gaggawa?” in ji shi.

Ndume ya ce babbar matsalarsa da ƙudurin ita ce lokacin da aka bijiro da ita, inda a cewarsa bai kamata a ce an kawo maganar ƙudurin ba a daidai wannan lokacin da ƴan Najeriya suke cikin ƙuncin rayuwa.

“Tun kakanninmu uuna biyan haraji a arewa. Don haka ba wai muna tsoron biyan haraji ba ne, duk wani ɗan ƙasa na ƙwarai zai biya haraji, amma gaskiya zuwa da wannan maganar a wannan lokacin bai dace ba,” in ji shi.

nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp