fidelitybank

NDLEA ta yi babban kamu a jihar Legas

Date:

Jami’an hukumar NDLEA mai yaƙi da shan miyagun ƙwayoyi, ta ce, ta kama mutum huɗu da ake zargi da hannu wajen safarar haramtattun ƙwayoyi masu nauyin 16,000kg a Jihar Legas.

Ana zargin mutanen – maza biyu da mata biyu – da safarar ƙwayoyi daga ƙasar Netherlands, a cewar kakakin NDLEA, Femi Babafemi.

A cewarsa, jami’an NDLEA sun shafe makonni suna bin sawun Aro Aderinde mai shekara 48, inda suka kama shi da zargin shigar da ganyen wiwi mai nauyin 3,149kg ta hanyar ɓoye shi a cikin ganyen kwakwa wanda aka zuba a kwantena mai lamba MSKU 1820587.

A gefe guda kuma, an kama mata biyu – Hauwawu Bashiru and Basirat Adebisi Yahaya – da zargin yunƙurin fitar da ƙwayar methamphetamine mai nauyin 90kg bisa haɗin gwiwa da wani fasto mai suna Anietie Okon Effiong mazaunin Jihar Akwa Ibom kuma aka kai su Uyo don fuskantar shari’a.

Haka nan, an kama wani da ake zargi da dillancin ƙwaya mai suna Monday Michael mai shekara 45 lokacin da yake ɗauke da ganyen wiwi mai nauyin 365kg cikin mota biyu a Legas.

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp