fidelitybank

NDLEA ta yi babban kamu a filin jirgin sama naLegas

Date:

Hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi NDLEA ta ce, ta kama ƙwayar Tramadol kusan miliyan biyu tare da maganin tari na Codeine a filin jirgin sama na Muratala Muhammad da ke Legas.

Wata sanarwa da hukumar ta fitar a yau Laraba ta ce, an shigar da ƙwayoyin ne daga Pakistan da kuma Birtaniya.

Ta ƙara da cewa, an ƙwace kayan a ranar 10 ga watan Maris, inda aka samu ƙwaya samfurin Co-codamol 349,800 wadda gwamnati ta haramta.

Sai kuma a ranar 15 ga Maris, inda jami’an NDLEA tare da haɗin gwiwar na Kwastam suka kama ƙwayar Tramadol 1,584,000 a filin jirgin.

A gefe guda kuma, NDLEA ta kama wani ɗan shekara 50 da yunƙurin shigar da hodar ibilis mai nauyin 11.91kg zuwa Ghana ta kan iyakar Seme da ke Legas.

A cewar sanarwar, waɗanda suka yi safarar ƙwayoyin sun yi amfani da motar jigilar kaya ta cikin filin jirgi mai suna Skyway Aviation Handling Compnay (SAHCO).

bbc news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...
X whatsapp