fidelitybank

NDLEA ta yi babban kamu a filin jirgin sama na Legas

Date:

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, ta kama wasu kayayyaki na Colorado da aka boye a cikin motocin da aka shigo da su daga birnin Montreal na kasar Canada a tashar jirgin ruwa ta Tincan, Apapa da filin jirgin sama na Murtala Muhammed International Airport, (MMIA), Ikeja, Legas.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan yada labarai da bayar da shawarwari na NDLEA Mista Femi Babafemi ya fitar ranar Lahadi a Abuja.

Babafemi ya ce magungunan da aka boye a cikin fakitin ruwan tabar wiwi da aka shigo da su daga kasar Afirka ta Kudu, an shirya su ne domin rarraba su gabanin bukukuwan Kirsimeti.

Ya ce an kama buhunan tabar wiwi 185, wanda aka fi sani da Colorado mai nauyin kilogiram 61.3 a wani gwajin hadin gwiwa na wani kwantena a tashar ruwan Tincan, Legas.

Ya kuma ce an ayyana kwantena mai lamba MSCU5206726 daga Montreal, Canada a matsayin mai dauke da motoci guda uku da aka yi amfani da su.

“Amma a gwajin da aka yi 100%, an gano cewa akwai motoci guda biyu; Motar Toyota Corolla ta 2009 da motar bas ta Ford Econoline ta 2009 da kuma injinan mota da kekuna da takalmi da sauran kayayyaki da suka hada da magungunan.

“Tuni ma’aikatan tashar ruwa guda biyu Abdulquadri Abdulazeez da Ogbuji Kenneth suna hannun hukumar NDLEA bisa zargin kamasu da jami’an tsaron tashar jiragen ruwa da ‘yan sanda suka yi a farko,” inji shi.

A halin da ake ciki, Babafemi ya ce, binciken da aka yi na hadakar kaya daga kasar Afirka ta Kudu ya kai ga gano ruwan tabar wiwi da aka yi fasa-kwaurin, mai nauyin kilogiram 16.50 a ranar 21 ga watan Disamba.

Ya ce hakan ya faru ne a dakin saukar jiragen sama na Skyway Aviation Handling Company Plc (SAHCO) na filin jirgin saman Legas.

“Binciken da jami’an yaki da muggan kwayoyi suka yi ya kai ga kama wasu jami’an dakon kaya guda hudu: Soremekun Olalekan Wasiu; Olufisayo Dayo; Moruf Olusegun Bashir da Imole Moses Ajayi.

jalingo news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp