Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, ta kara jaddada aniyarta na yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi a Najeriya, inda ta yaye jamiāanta 650 na rundunar a Makarantar Sojojin Najeriya (NASI) Jaji, Jihar Kaduna bayan ta kwashe makonni ta na horo na musamman.
Rundunar na daya daga cikin dabarar da NDLEA ta kirkira na shekarar 2021, domin kara karfi da manufa a kokarinta na rage samar da magunguna ta hanyar ba da kariya ga jami’ai da maza na NDLEA wadanda dole ne su yi aiki a cikin yanayi mai hadari yayin gudanar da ayyukansu.
Da yake jawabi a wurin bikin, Shugaban Hukumar NDLEA, Brig. Janar Mohamed Buba Marwa (Mai Ritaya) ya ce, horon na musamman zai karawa jamiāan kwarin gwiwar gudanar da ayyukansu na musamman da suke baiwa hukumar wajen yaki da miyagun kwayoyi.
Ya ce, āYa na da mahimmanci in tunatar da ku cewa yayin da Hukumar ta inganta ayyukanta na yaki da fataucin miyagun kwayoyi, hidimar ku za ta kara zama mai matukar muhimmanci, domin cimma nasarar manufofin hukumar mu. Yanayin horon ku na musamman ya na buĘatar ku zama mai haÉaka Ęarfi ga ma’aikatan NDLEA na yau da kullun a fagen.
āBa ni da tantama cewa, za ku iya biyan bukatar aikin, saboda tsararrun sojoji da jamiāan tsaro sun wuce wannan kwas kuma sun bambanta a fagen, rahoton ci gaban da na samu, gami da tantancewa a nan gaba, ya tabbatar da cewa an cimma manufar kwas din. Domin haka yayin da kuke kammala karatunku a yau, ina kira gare ku da kada ku huta saboda za a gwada kwarewar ku daga lokaci zuwa lokaci ta hanyar kalubale da za su sake faruwa a cikin aikinku na masu yaki da muggan kwayoyi,ā inji shi.ba cewar The Nation.