fidelitybank

NDLEA ta tursasa wani Ɗan Kasuwa ya yi kashi har sau huɗu sannan ya fitar da hodar Ibilis 88 a cikin sa

Date:

Jami’an hukumar yaki da masu ta’ammali da miyagun kwayoyi ta NDLEA, sun kama wani fasinja a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe International Airport, da ke Abuja bayan da aka gano yana da alamun koken a cikinsa.

A wata sanarwa da kakakin hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi, ya fitar yau Lahadi, ya ce mutumin, Paul Okwuy Mbadugha, mai shekar 54, wanda dan kasuwa ne da zai tafi Vietnam, ya shiga hannun hukumar ne a ranar Litinin 12 ga watan Agustan nan na 2024, yayin da yake shirin hawa jirgin Qatar Airways zuwa Vietnam, bayan yada zango a Doha.

Sanarwar ta kara da cewa: ”Bayan kwana hudu da aka sanya shi yana bahaya, Mbadugha ya kasayar da kullin koken 88 da nauyinsu ya kai kilgram 1.171.

Hukumar ta ce, a bahasin da mutumin ya bayar ya ce, shi dan kasuwa ne a Lagos kuma wani abokinsa ne a Isolo, ya ba shi kullin ya hadiye domin kaiwa Vietnam a kan kudi dala 2,000.

Haka kuma hukumar ta NDLEA ta ce, jami’ant sun kama wani babban kulli na na ganyen wiwi da nauyinsa ya kai kilogram 800, da aka boye a kwalayen taliyar yara, da nufin kaiwa kasar Kongo.

Hukumar ta ce, bayn da aka bi diddigin inda kayan ya fito an kama wani mutum mai suna Nnamani Sunday Sunny a kasuwar Alaba International market, a yankin karamar hukumar Ojo, a Lagos.

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp