fidelitybank

NDLEA ta tursasa wani Ɗan Kasuwa ya yi kashi har sau huɗu sannan ya fitar da hodar Ibilis 88 a cikin sa

Date:

Jami’an hukumar yaki da masu ta’ammali da miyagun kwayoyi ta NDLEA, sun kama wani fasinja a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe International Airport, da ke Abuja bayan da aka gano yana da alamun koken a cikinsa.

A wata sanarwa da kakakin hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi, ya fitar yau Lahadi, ya ce mutumin, Paul Okwuy Mbadugha, mai shekar 54, wanda dan kasuwa ne da zai tafi Vietnam, ya shiga hannun hukumar ne a ranar Litinin 12 ga watan Agustan nan na 2024, yayin da yake shirin hawa jirgin Qatar Airways zuwa Vietnam, bayan yada zango a Doha.

Sanarwar ta kara da cewa: ”Bayan kwana hudu da aka sanya shi yana bahaya, Mbadugha ya kasayar da kullin koken 88 da nauyinsu ya kai kilgram 1.171.

Hukumar ta ce, a bahasin da mutumin ya bayar ya ce, shi dan kasuwa ne a Lagos kuma wani abokinsa ne a Isolo, ya ba shi kullin ya hadiye domin kaiwa Vietnam a kan kudi dala 2,000.

Haka kuma hukumar ta NDLEA ta ce, jami’ant sun kama wani babban kulli na na ganyen wiwi da nauyinsa ya kai kilogram 800, da aka boye a kwalayen taliyar yara, da nufin kaiwa kasar Kongo.

Hukumar ta ce, bayn da aka bi diddigin inda kayan ya fito an kama wani mutum mai suna Nnamani Sunday Sunny a kasuwar Alaba International market, a yankin karamar hukumar Ojo, a Lagos.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp