Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta NDLEA, ta yi martani a kan kalaman babban Sifeto Janar na ‘yan sandan kasar nan, inda ya yi kira ga a hukunta jami’an hukumar da suke taimakawa wajen shigo da hodar Iblis Najeriya.
Zaku tuna cewa a ranar Litinin hukumar NDLEA ta garkame dakataccen DCP na yan sanda, Abba Kyari, kan laifin safarar hodar Iblis mai nauyin kilo 25.
Sifeto Janar na ‘yan sanda, IGP Usman Baba Alkali, ya yi kira ga Shugaban hukumar NDLE a yau Talata cewa, ta damke jami’ansa dake taimakawa masu safarar kwaya tare da Abba Kyari.
Daily Trust ta rawaito kakakin hukumar, Femi Babafemi, ya ce, hukumar ba za ta yi wani rufa-rufa ba, ko wanene sai an tona masa asiri.
Yayin da aka tambaye shi shin me ya sa ba’a ambaci sunayen jami’an NDLEA da su ka yi safarar tare da Abba Kyari ba, Babafemi ya ce hukumar ba za ta boye kowa ba.