fidelitybank

NDLEA ta lalata ganyen Wiwi kilo 7,286 a Edo

Date:

Gabanin babban zaɓen 2023 da ke tafe a ranar Asabar, jami’an Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta NDLEA, ta bayyana lalata ganye mai sa maye mai nauyin kilogiram 7,286 bayan yin dirar miƙiya a wani gandun dajin Ujiogba da ke jihar Edo.

A wata sanarwa da darektan yaɗa labaru na hukumar ya fitar a shafinta na twita, ya ce ta gudanar da samamen ne a ranar Laraba bayan samun bayanan sirri da ke cewa masu tu’ammali da kwayoyi sun shiga dajin rike da ɗaruruwan jakukkunan ganyen domin rarrabawa zuwa wasu jihohi gabanin gudanar da zaɓen.

Karanta Wannan: NDLEA ta kama hodar ibilis da za a mika kasashen waje

NDLEA ta ce sai da jami’anta suka shafe tsawon lokaci suna artabu da ‘yan bindiga da kuma manya masu safarar ƙwayoyi kafin ta samu nasara a kansu, inda bayan nan ta cinna wuta kan wasu jakukkunan tabar wiwi da dama, tare kuma da tafiya da wasu guda bakwai domin gudanar da bincike da hukunta waɗanda ake zargi.

Ta kuma ce ta ƙwato bindiga ƙirar AK47 da wasu ƙananan bindigogi da kuma harsasai, inda suka kama wani ɗan shekara 24 mai suna Calvary Essien da ake zargi da tu’ammali da miyagun ƙwayoyin.

Da yake mayar da martani, shugaban hukumar, Birgediya-Janar Buba Marwa mai ritaya, ya yaba wa jami’an da suka gudanar da samamen da kuma wasu kusan 10,000 da aka tura zuwa faɗin jihohi domin sa ido gabanin zaɓe wajen ganin ‘yan bangar siyasa basu yi amfani da ƙwayoyi ba kafin da lokaci da kuma bayan zaɓe.

ng news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp