fidelitybank

NDLEA ta kama ƙwayoyi mai nauyin tan 2.1 a Kano

Date:

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, ta kama wasu mutane 352 da ake zargi tare da kama tan 2.1 na haramtattun kwayoyi a jihar Kano.

Kwamandan NDLEA a jihar, Abubakar Idris-Ahmad, ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na (NAN) a Kano ranar Alhamis.

Idris-Ahmad ya ce, an kama mutanen ne a tsakanin watan Janairu zuwa Maris.

Ya ce wadanda ake zargin sun hada da maza 208 da mata 44, yayin da magungunan da aka kama sun hada da kilogiram 955.304 na tabar wiwi, da Codeine da Tramadol kilogiram 1,225.05.

Sauran a cewarsa, sun hada da gram 25 na hodar iblis, gram 17 na tabar heroin da gram 52 na methamphetamine.

Kwamandan ya ce babban kalubalen da ke gaban hukumar a jihar shi ne shawo kan al’umma wajen bankado masu safarar miyagun kwayoyi a tsakaninsu.

“Kalubalen mu shine samun damar ilimantar da al’umma don samar da bayanai masu amfani game da maboyar masu amfani da muggan kwayoyi ko dillalan da ayyukansu suka ci gaba da yin illa ga al’umma.

“Ya kamata jama’a su lura da illolin da masu shan muggan kwayoyi ko masu safarar miyagun kwayoyi ke haifarwa a cikin al’umma ta yadda jama’a za su fito da bayanai masu amfani don tabbatar da al’ummar da ba ta da miyagun kwayoyi,” inji Idris-Ahmad.

Don haka ya yi kira ga jama’a da su rika bayar da bayanai masu amfani kuma a kan lokaci kan masu safarar miyagun kwayoyi ga rundunar, ta yadda za a fitar da su daga yawo da kuma kare al’umma.

nigeria news(punch)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Turji ya saki Mutane 32 bayan zaman sulhu

Shahararren shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, ya saki mutane...

ADC ta gargadi El’Rufa’i kan ruguza jam’iyyar

Shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kaduna,...

An gindayawa Thomas Partey sharudan beli

An gindaya sharuddan belin tsohon dan wasan tsakiya na...

Fursunoni 37 na jiran zartas musu da hukuncin kisa a Bauchi

Fursunoni 37 da aka yanke wa hukuncin kisa bisa...

Kwamitin sulhu na MDD zai gana kan makomar ƴan Isra’ila da ke hannun Hamas

Kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya zai tattauna yau...

Sojoji sun kashe ‘yan Boko Haram 17 a Borno da Adamawa

Sojoji da ke aiki ƙarƙashin rundunar Operation Haɗin Kai...

Falana ya caccaki Tinubu kan salon tattalin arzikin Najeriya

Fitaccen lauyan nan mai kare haƙƙin bil adama, Femi...

Yahudawa sun yiwa Netanyahu tutsu kan mamaye Gaza

Ƴan'uwan Isra'ilawan da aka yi garkuwa da su a...

Cin zarafin Daliba ya sanya yin zanga-zanga a China

Zanga-zanga ta ɓarke a kudancin China sakamakon cin zarafin...

Tinubu ya baiwa ‘yan wasan kwallon kwando dala dubu 100 da filaye a Abuja

Gwamnatin Tarayya ta karrama kungiyar kwallon kwando ta mata...

‘Yan siyasa na kara matsin lamba Jonathan ya fito takara a 2027 – Bashir

Tsohon mai taimaka wa tsohon shugaban kasa kan harkokin...

Gwamnati ta karbi tawagar ‘yan wasan kwallon kwando D’Tigress

Tawagar ƴan wasan ƙwallon kwando mata ta Najeriya ta...
X whatsapp