fidelitybank

NDLEA ta kama tsoho da tabar wiwi da mai safarar kwayoyi a Kano

Date:

Jami’an hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, sun kama wani Dattijo mai suna Aliyu Adebiyi dan shekara 67, wanda a gidansa suka gano tabar wiwi kilogiram 234 a kauyen Sokoto, Owena Ijesa, a karamar hukumar Atakumosa ta Gabas ta jihar Osun. Kakakin hukumar Femi Babafemi ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi a Abuja.

A cewarsa, wanda ake zargin, a cikin bayaninsa, ya ce, wani dillalin miyagun kwayoyi ya ajiye kayan a wurinsa akan kudi naira 6,000 duk wata kuma ya biya na tsawon watanni uku a gaba.

Hakazalika, an kama wani kuturu da ya yi kaurin suna wajen safarar miyagun kwayoyi, Haruna Abdullahi, mai shekaru 45 a garin Garko, jihar Kano a ranar Alhamis 19 ga watan Janairu, yayin da aka kwato kilogiram 2.2 na tabar wiwi da Diazepam da Exol daban-daban daga gare shi.

Moreso, Babafemi ya kuma bayyana cewa, an sake samun ci gaba a kokarin da ake yi na shigo da hodar iblis da skunk 126.95kgs cikin Najeriya da aka boye a cikin buhunan shayi na ganye da kuma motocin da ke shigowa da su daga Brazil da Canada a filin jirgin saman Akanu Ibiam International Airport (AIIA), Enugu da kuma Jami’an NDLEA na tashar jirgin ruwan Tincan dake Legas.

ā€œA filin jirgin saman Enugu, an kama wani fasinja mai suna Eze Christian Ikenna, dan shekara 42, wanda ya shiga wani jirgin saman Ethiopian Airline da ya taho daga Brazil ta hanyar Addis Ababa, Habasha, lokacin da ya isa filin jirgin da karfe 12:30 na ranar Juma’a, 20 ga watan Janairu. A binciken da aka yi wa buhunan sa guda biyu, an gano manyan buhuna guda 19 da ya yi ikirarin cewa suna dauke da shayin ganye amma daga baya aka gano cewa hodar iblis ce mai nauyin kilogiram 16.20,ā€ inji shi.

nigerianewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaʙi da fataucin miyagun ʙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ʙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miʙa saʙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaʙalar belin Danwawu,...
X whatsapp