fidelitybank

NDLEA ta kama tsoho da tabar wiwi da mai safarar kwayoyi a Kano

Date:

Jami’an hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, sun kama wani Dattijo mai suna Aliyu Adebiyi dan shekara 67, wanda a gidansa suka gano tabar wiwi kilogiram 234 a kauyen Sokoto, Owena Ijesa, a karamar hukumar Atakumosa ta Gabas ta jihar Osun. Kakakin hukumar Femi Babafemi ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi a Abuja.

A cewarsa, wanda ake zargin, a cikin bayaninsa, ya ce, wani dillalin miyagun kwayoyi ya ajiye kayan a wurinsa akan kudi naira 6,000 duk wata kuma ya biya na tsawon watanni uku a gaba.

Hakazalika, an kama wani kuturu da ya yi kaurin suna wajen safarar miyagun kwayoyi, Haruna Abdullahi, mai shekaru 45 a garin Garko, jihar Kano a ranar Alhamis 19 ga watan Janairu, yayin da aka kwato kilogiram 2.2 na tabar wiwi da Diazepam da Exol daban-daban daga gare shi.

Moreso, Babafemi ya kuma bayyana cewa, an sake samun ci gaba a kokarin da ake yi na shigo da hodar iblis da skunk 126.95kgs cikin Najeriya da aka boye a cikin buhunan shayi na ganye da kuma motocin da ke shigowa da su daga Brazil da Canada a filin jirgin saman Akanu Ibiam International Airport (AIIA), Enugu da kuma Jami’an NDLEA na tashar jirgin ruwan Tincan dake Legas.

ā€œA filin jirgin saman Enugu, an kama wani fasinja mai suna Eze Christian Ikenna, dan shekara 42, wanda ya shiga wani jirgin saman Ethiopian Airline da ya taho daga Brazil ta hanyar Addis Ababa, Habasha, lokacin da ya isa filin jirgin da karfe 12:30 na ranar Juma’a, 20 ga watan Janairu. A binciken da aka yi wa buhunan sa guda biyu, an gano manyan buhuna guda 19 da ya yi ikirarin cewa suna dauke da shayin ganye amma daga baya aka gano cewa hodar iblis ce mai nauyin kilogiram 16.20,ā€ inji shi.

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaʙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ʙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ʙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaʙi...

Najeriya za ta kwashe Ę“an ʙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ʙasar...

Iran ta ʙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ʙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ʙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ʓansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ʙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Ę“an ʙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ā€˜yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ʙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin Ę“anbindiga da suka addabi yankunan ʙaramar...
X whatsapp