Jami’an hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, sun kama akalla tan 6,668 na haramtattun abubuwa cikin shekaru biyu.
Wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi ya fitar ranar Juma’a, ta bayyana cewa hukumar ta kama sama da mutane 36,096 da ake tuhuma tare da gurfanar da sama da 6,043 a cikin wannan lokaci.
A cewar sanarwar, “Shugaban hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi, Brig. Janar Buba Marwa (Rtd), ya bayyana hakan ne a lokacin da yake amsa bukatar hadin gwiwa tare da tura karin jami’an NDLEA a dukkan sassan jihar Katsina da Gwamna Dikko Radda ya yi domin shawo kan matsalar shaye-shayen miyagun kwayoyi.”
“Hadarin shaye-shaye babban lamari ne kuma ya lalata rayuwar matasanmu da al’ummarmu. Shi ne makiyin jama’a na daya, musamman ma bangaren aikata laifuka. Kashi 99 cikin 100 na masu laifi dole ne su fara amfani da kwayoyi kuma su kasance karkashin ikon aikata wasu ayyukansu.
“Don haka ne hukumar ta NDLEA karkashin hadin guiwar hukumomin da hukumar ta yi duk kokarin da take yi wajen ganin an aiwatar da ‘mummunan mataki’. .
“Sama da tan 6,668 na haramtattun abubuwa an kama su a cikin shekaru biyu, kuma muna ba da tabbacin cewa za mu ci gaba da aiki tukuru har sai an tsaftace tituna daga shan miyagun kwayoyi. Wannan shi ne bangaren rage samar da magunguna, inda muka kama wadanda suka aikata wannan aika-aika, kuma an kama sama da mutane 36,096 da ake tuhuma, sama da 6,043 kuma an gurfanar da su gaban kuliya tare da hukunta su a cikin wannan lokaci.”